IQNA

An Fitar Da Adadin Karshe Na Mutanaen da suka Mutu A Zanga-zangar Sudan

23:24 - April 27, 2019
Lambar Labari: 3483583
Ma'ikatar kiwon lafiya a Sudan ta fitr da adadi na karshe na wadanda suka mutu a zanga-zangar kasar, wanda ya kai mutane 53.

Kamfanin dillancin labaran iqna,

Ma’ikatar kiwon lafiya a kasar Sudan ta sanar ad adadi na karshe na wadanda suka rasa rayukansu a zanga-zangar da aka gudanara  kasar wadda ta kawo karshen mulkin Albashir.

A cikin bayanin da ta fitar a jiya, ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Sudan ta sanar da cewa, mutane 53 aka tabbatar da mutuwarsua  dukkanin fadin kasar, a zanga-zangar kin jinin gwamnatin hambararren shugaban kasar ta Sudan Umar Hassan Albashir.

Bayanin ya ce mafi yawan mutanen sun rasa rayukansu ne a yayin zanga-zangar, biyo bayan artabun da aka yi tsakaninsu da jami’an tsaro, yayin da kuma wasu suka rasu a asibiti sakamakon samun munanan raunuka.

Jami’an tsaron sun yi amfani da karfi wajen tarwatsa masu zanga-zangar, musammana  biranan Khartum da kuma Ummu Durman, da wasu yankuna a  cikin Darfur.

 

3806563

 

captcha