IQNA

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwa game da rikicin addini a kasar Habasha

21:19 - May 08, 2022
Lambar Labari: 3487265
Tehran (IQNA) Hukumar kare hakkin bil adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi game da kazamin fadan baya-bayan nan da aka yi tsakanin Musulmi da Kiristocin Orthodox a kasar Habasha tare da yin kira ga hukumomi da su gudanar da bincike.

Babbar jami'ar kare hakkin bil'adama ta Majalisar Dinkin Duniya Michelle Bachelet ta ce ta sanar da hakan, inda ta ce sun damu matuka da tashin hankalin da ya barke a arewacin kasar Habasha a karshen watan da ya gabata, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 30 tare da jikkata sama da 100.

A ranar 26 ga watan Afrilu ne aka fara arangama a garin Gonder da ke yankin Amhara dangane da wata takaddama kan filaye, daga nan sai fadan ya bazu zuwa wasu sassa na Addis Ababa babban birnin kasar Habasha.

Majalisar kula da harkokin addinin musulunci ta Amhara ta sanar da cewa an kai wa jana'izar wani musulmi hari, tare da bayyana lamarin a matsayin kisan kiyashi da "Kiristoci masu tsatsauran ra'ayi ke yi."

Makabartar da aka kai harin na kusa da wani masallaci da coci kuma ana ci gaba da samun tashe tashen hankula tsakanin Musulmi da Kiristocin Orthodox, wadanda suke  da rinjaye a kasar Habasha.

“Na san an kona masallatai biyu a Gandar, an kuma lalata wasu guda biyu,” in ji Bachelet a cikin wata sanarwa.

Ta kara da cewa: "Da alama bayan haka, a hare-haren ramuwar gayya, an kona wasu Kiristocin Orthodox guda biyu da suka mutu har lahira, an kuma yi wa wani mutum duka shi ma ya mutu har lahira, an kuma kona majami'u biyar a kudu maso yammacin kasar."

Baki daya, 'yan sanda sun kama akalla mutane 578 a akalla garuruwa hudu a rikicin, in ji hukumar kare hakkin bil'adama ta Majalisar Dinkin Duniya.

Bachelet ta ce "Ina kira ga mahukuntan Habasha da su gaggauta gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa da gaskiya a kan lamarin."

 

4055408

 

 

captcha