Shafin yada labarai na tashar Aljazeera ya bayar da rahoton cewa, bayan da sakamakon binciken ya tabbatar da cewa gwamnatin Isra’ila c eta aiwatar da kisan gillar da aka yi wa kananan yara 5 a yankin Jabalia da ke arewacin zirin Gaza, iyalan wadannan yara sun bukaci a gurfanar da mahukuntan Isra’ila a gaban kotu.
Wadannan yara sun yi shahada ne a harin baya-bayan nan da yahudawan sahyuniya suka kai a zirin Gaza.
Jaridar Haaretz ta bayyana a cikin wani rahoto cewa: A wancan lokaci sojojin Isra'ila sun yi ikirarin cewa an kashe wadannan yara ne sakamakon fadowar makamin roka na Saraya al-Quds (reshen soja na kungiyar Jihad Islami) a yankin Jabalia.
Iyalan yaran biyar kuma sun jaddada wajibcin gurfanar da firayi ministan Isra’ila kan wannan laifi a gaban kotun duniya, kasantuwar shi ne keda hannu kai tsaye wajen kai hare-haren.
A yayin wani taron manema labarai da suka gudanar a wurin janazar kananan yaran a sansanin Jabalia, iyalai da suka rasa rayukansu sun bukaci hukumar Palasdinawa da ta dauki nauyin shigar da wanan kara kan kisan kananan yara da Isra’ila ta yi.
Haka nan kuma iyalan wadannan yara sun yi Allawadai da yadda gwamnatocin kasashen larabawa suka yi gum da bakunansu kan wannan mummunar ta’asa da Isra’ila ta aikata, da kuma yadda wasunsu ma suke ta hankoron ganin sun kulla hulda da Isra’ila a cikin irin wannan yanayi.