IQNA

Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi Ta Mayar Wa Macron Da Martani

23:51 - October 12, 2020
Lambar Labari: 3485268
Tehran (IQNA) kungiyar kasashen musulmi ta mayar wa shugaban kasar Faransa Emmnuel Macron da martani dangane da kalamansa na kyamar musulunci.

Shafin yada labarai Sada ya bayar da rahoton cewa, babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi Muhammad Al-Isa ya mayarwa Macron da martani da cewa, addinin musulunci sako ne na ubangiji, wanda babu wani abu na kaucewa a cikinsa.

Ya ce babu mai musu kan cewa akwai wasu daga cikin musulmi da suke fahimtar addini a birkice, wanda hakan ne ke kais u ga aikata ayyukan ta’addanci da sunan addini, amma ba addinin ne ya koyar da su ta’addanci, domin kuwa babu ta’addanci a cikin addinin musulunci.

Ya ci gaba da cewa, ba adalci ba ne a yanke hukunci a kan addinin musulunci da ayyukan da wasu masu tsatsauran ra’ayi da da ba su fahimci koyarwar musulunci ba, domin kuwa a cikin kowane addini ana samun hakan, kuma adalci ba ne a hukunta kowane addini da ayyukan irin wadannan mutane.

A cikin ‘yan kwanakin nan ne dai shuban kasar ta Faransa yay i kalamai na nuna kyama ga musulmi, tare da bayyana su a matsayin babban hadari ga makomar kasar Faransa saboda ayyukan ta’addanci.

3928732

 

 

 

 

captcha