Shafin yada labarai na jagoran juyin juya halin musulunci a Iran ya bayar da bayanin cewa, a daren jiya an gudanar da zaman juyayia daren Tasu'a a Husainiyar Imam Khomeini tare da halartar jagoran juyi na Iran.
Hojjatol Islam Sa'adi ne ya gabatar da jawabi a wurin, inda ya mayar da hankali kan abubuwan da suka faru a ranar Tasu'a ga Imam Hussain (AS) da sahabbansa da kuma zuriyar manzon Allah (SAW) da suke tare da shi, inda ya bayyana tsayin dakan da suka yi a wannan rana shi ne babban sirrin nasararsu a ranar Ashura.
Kamar sauran kwanakin da suka gabata an takaita halartar jama'a a wurin taron, sakamakon matsaloli na kiwon lafiya da ake fama da su a wannan lokaci.